fidelitybank

A gaggauta sanya dokar ta ɓaci a ɓangaren ta’ammali da ƙwayoyi – Ƙungiyar Matan Gwamnoni

Date:

Kungiyar matan gwamnonin kasar nan sun bukaci gwamnatin tarayya da na jihohi da su ayyana dokar ta-baci a kan bangaren shaye-shayen miyagun kwayoyi da safarar su da nufin hada karfi da karfe domin shawo kan matsalar.

Kungiyar ta yi wannan kiran ne a ranar Talatar nan a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun shugabar kungiyar kuma uwargidan gwamnan jihar Kwara, Ambasada Olufolake Abdulrasaq.

Wannan ci gaban ya biyo bayan kammala wani horon kwanaki biyu da hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa ta shirya wa matan gwamnonin a Abuja.

Wata sanarwa da Daraktan Yada Labarai na Hukumar NDLEA Femi Babafemi ya fitar a ranar Talata, ta ce, matan gwamnonin sun amince da bukatar gaggawar karbe iko tare da sake karfafa kwamitocin yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi domin gudanar da ingantattun ayyuka jihohin kasar nan.

Sun jaddada bukatar Gwamnatin Tarayya da Gwamnonin Jihohi da su ayyana dokar ta-baci a kan amfani da miyagun kwayoyi da kuma fataucin miyagun kwayoyi da nufin samar da kayan aiki domin tunkarar kalubalen.

leadership news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp