fidelitybank

A gaggauta sakin shugaban mu – Kungiyar Kwadago

Date:

Ƙungiyar kwadago ta Najeriya NLC ta buƙaci hukumomin ƙasar su gaggauta sakin shugabanta ba tare da wani sharaɗi ba.

Da safiyar ranar Litinin ne hukumar tsaro ta farin kaya DSS ta kama Mista Ajaero a filin jirgin saman Abuja, lokacin da yake kan hanyarsa ta zuwa Birtaniya domin halartar taron ƙungiyar kwadago TUC, ta Birtnaiya

Cikin wata sanarwa da shugaban sashen yaɗa labarai da hulɗa da jama’a na ƙungiyar, Benson Upah ya fitar, ya ce ta sanya rassanta na jihohi da manyan ƙungiyoyin da ke ƙawance da ita cikin shirin ko-ta-kwana, kan lamarin da ta kira mai ”tayar da hankali”.

“Ƙungiyarmu ba za ta zuba ido tana ganin ana tozarta shugabanni da mambobinta ba, don haka muke buƙatar a gaggauta sakin Kwamared Ajaero, ba tare da gindaya kowane irin sharaɗi ba”, kamar yadda sanarwar ta yi ƙarin haske..

Sanarwar ta ci gaba da cewa ”an tsare mista Ajaero a wani wuri da ba a sani ba, don haka ba a san halin da lafiyarsa ke ciki ba, duk wani yunƙuri na jin halin da yake ciki ya ci-tura”.

NLC ta kuma ce yanzu haka ta shiga taron sirri da manyan shugabanninta, tana mai cewa za ta bayyana wa duniya abin da tattauna da zarar ta kammala.

sspdf news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp