fidelitybank

A gaggauta matakan kariya a sufurin ruwa – Buhari

Date:

Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya bayar da umarnin sake yin duba don inganta matakan kiyaye afkuwar haɗurra a tsarin sufurin ruwa na ƙasar, sakamakon hatsarin wani kwale-kwale da ya yi sanadin mutuwar gomman mutane a jihar Anambra.

An samu rahotanni masu cin karo da juna kan ainihin yawan waɗanda abin ya rutsa da su a jihar da ke kudu maso gabashin Najeriya.

Amma wata sanarwa da mai taimaka wa Buhari kan yada labarai ta ce, ana jiran bayanai har yanzu, sai dai hukumimin agaji sun tabbatar d acewa “yawan waɗanda suka mutu ya kai 76.”

Yawancin waɗanda suka rasun dai mata ne da yara da suke ƙoƙarin tsere wa yankinsu da ambaliyar ruwa ta mamaye.

Rahotanni sun ce jirgin wanda ke ɗauke da mutum fiye da 80 ya yi hatsarin ne a yankin Ogbaru a ranar Juma’a.

Jami’ai sun ɗora alhakin jawo hatsarin kan injin jirgin da suka ce ya lalace, sannan kuma jirgin ya yi karo da wata gada.

Shugaba Buhari ya miƙa saƙon ta’aziyyarsa ga iyalan waɗanda abin ya rutsa da su, yana mai bayyana hatsarin a matsayin mummuna, sannan ya ƙara da cewa dole ne hukumomi su yi duk abin da ya dace don gano waɗanda har yanzu ba a gansu ba.

Kazalika shugaban ya bai wa hukumomin gwamnati umarnin sake yin nazari kan tsarin tabbatar da tsaro a sufurin jiragen ruwa da kwale-kwale don kare afkuwar irin hakan a gaba.

Ana yawan samun hatsarin kwale-kwale a Najeriya – inda a mafi yawan lokuta ake ɗora alhakin hakan kan ɗaukar mutanen da suka fi ƙarfin jirgin da sauran matsaloli.

besda salary

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp