fidelitybank

A gaggauta korar wasu alkalai uku a kasar nan – Majalisar Harkokin Shari’a

Date:

Majalisar kula da harkokin shari’a a kasar nan, ta bayar da shawarar yi wa wasu manyan alƙalai biyu ritaya saboda laifin yin ƙarya a shekarunsu na haihuwa.

Cikin wata sanarwa a ranar Juma’a, National Judicial Council (NJC) ta ce ta gano Alƙalin Alƙlai na jihar Imo T. E. Chukwuemeka Chikeka, da shugaban kotunan shari’ar Musulunci na jihar Yobe Babagana Mahdi sun aikata laifi.

Haka nan majalisar ta ɗauki mataki kan wasu alƙalan da suka haɗa da na yin gargaɗi, da hana su albashi, da kuma saka musu ido bisa laifuka daban-daban da suka aikata.

A cewar sanarwar, binciken NJC ya gano alƙalin alƙalan na Imo na da ranakun haihuwa biyu na 27 ga watan Oktoban 1956 da 27 ga Oktoban 1958, yayin da shi kuma shugaban kotunan shari’a na Yobe yake da kwanan wata har uku daban-daban.

Bisa wannan dalili ne majalisar ta ce ta bai wa gwamnatin jihar Imo da ke kudancin Najeriya shawarar yi wa Mai Shari’a Chikeka ritayar dole tare da ƙwace albashin da ya karɓa tun daga ranar 21 ga watan Oktoban 2021.

Kazalika, majalisar ta bai wa gwamnatin jihar Yobe shawarar yi wa Mai Shari’a Babagana Mahadi ritaya ta tilas, wadda ya kamata ya yi tun shekara 12 da suka wuce, sannan kuma ya dawo da albashin da ya karɓa na tsawon waɗannan shekarun.

Duk da cewa an fara gudanar da binciken tun kafin shugabar majalisar kuma alƙaliyar alƙalai ta Najeriya Kekere-Ekun ta samu muƙamin, matakan sun yi daidai da alwashin da ta ɗauka na dawo kima da martabar ɓangaren shari’a a Najeriya.

Lamarin na zuwa ne yayin da ƙungiyoyi da ‘yan gwagwarmaya ke caccakar Ministan Abuja Nyesom Wike saboda bai wa wasu alƙalai 40 kyautar gidaje, abin da ya ce manufa ce ta gwamnatin Bola Tinubu yake aiwatarwa.

daily sun news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp