fidelitybank

A gaggauta korar wasu alkalai uku a kasar nan – Majalisar Harkokin Shari’a

Date:

Majalisar kula da harkokin shari’a a kasar nan, ta bayar da shawarar yi wa wasu manyan alƙalai biyu ritaya saboda laifin yin ƙarya a shekarunsu na haihuwa.

Cikin wata sanarwa a ranar Juma’a, National Judicial Council (NJC) ta ce ta gano Alƙalin Alƙlai na jihar Imo T. E. Chukwuemeka Chikeka, da shugaban kotunan shari’ar Musulunci na jihar Yobe Babagana Mahdi sun aikata laifi.

Haka nan majalisar ta ɗauki mataki kan wasu alƙalan da suka haɗa da na yin gargaɗi, da hana su albashi, da kuma saka musu ido bisa laifuka daban-daban da suka aikata.

A cewar sanarwar, binciken NJC ya gano alƙalin alƙalan na Imo na da ranakun haihuwa biyu na 27 ga watan Oktoban 1956 da 27 ga Oktoban 1958, yayin da shi kuma shugaban kotunan shari’a na Yobe yake da kwanan wata har uku daban-daban.

Bisa wannan dalili ne majalisar ta ce ta bai wa gwamnatin jihar Imo da ke kudancin Najeriya shawarar yi wa Mai Shari’a Chikeka ritayar dole tare da ƙwace albashin da ya karɓa tun daga ranar 21 ga watan Oktoban 2021.

Kazalika, majalisar ta bai wa gwamnatin jihar Yobe shawarar yi wa Mai Shari’a Babagana Mahadi ritaya ta tilas, wadda ya kamata ya yi tun shekara 12 da suka wuce, sannan kuma ya dawo da albashin da ya karɓa na tsawon waɗannan shekarun.

Duk da cewa an fara gudanar da binciken tun kafin shugabar majalisar kuma alƙaliyar alƙalai ta Najeriya Kekere-Ekun ta samu muƙamin, matakan sun yi daidai da alwashin da ta ɗauka na dawo kima da martabar ɓangaren shari’a a Najeriya.

Lamarin na zuwa ne yayin da ƙungiyoyi da ‘yan gwagwarmaya ke caccakar Ministan Abuja Nyesom Wike saboda bai wa wasu alƙalai 40 kyautar gidaje, abin da ya ce manufa ce ta gwamnatin Bola Tinubu yake aiwatarwa.

the punch newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp