fidelitybank

A gaggauta kawo karshen rashin jituwa tsakanin Najeriya da Dubai – Tinubu

Date:

Shugaban Kasa Bola Tinubu, ya yi kira da a gaggauta kawo ƙarshen rashin jituwar da ke tsakanin ƙasar da Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa, wanda ya shafi jigilar jirage da bayar da biza takanin ƙasashen biyu.

Tinubu ya yi kiran ne a lokacin da ya karɓi baƙuncin jakadan UAE a Najeriya Ambassador, Salem Saeed Al-Shamsi a fadarsa da ke Abuja.

A shekarar da ta gabata ne UAE ta dakatar da bayar da biza ga ‘yan Najeriya bayan da kamfanin jirgin sama na Emirates ya dakatar da jigila a Najeriya saboda hana shi wasu haƙƙoƙinsa, saboda wasu ƙa’idoji na kuɗaɗen ƙasashen waje.

Kamfanin ya ce ya ɗauki matakin ne bayan duk wani yunƙuri da ya yi na warware matsalar da hukumomin Najeriya ta hanyar lalama ya ci tura.

Shugaba Tinubu ya ce ya kamata a gaggauta warware matsalar, yana mai cewa a shirye yake ya shiga tsakani da kansa, don kawo ƙarshen matsalar.

“Mu kalli abin a matsayin saɓani na ‘yan uwataka, domin mu warware shi cikin sauki, dole mu yi aiki tare, Muna buƙatar amincewa da dokokin bai daya kan jigilar jiragen sama da batun ‘yan ci-rani,” in ji Tinubu

nigerianewspapers.com.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp