Majalisar wakilai ta bukaci ma’aikatar albarkatun ruwa da ta dauki dukkannin matakan da ya dace domin kammala aikin gyaran madatsar ruwa da ke garin Faki a karamar Hukumar Ikara da ke jihar Kaduna.
Bukatar hakan na kunshe a cikin wani kudiri da dan Majalisar mai wakiltar mazabar Ikara da Kubau, Dr. Hamisu Ibrahim Kubau, ya gabatar a zaman majalisar na ranar al’hamis.
Da ya ke gabatar da kudirin Dr. Hamisu Ibrahim Kubau, ya ce tun a shekara ta 2003 ne a ka bada kwangilar gyaran madatsar ruwa ta Paki, sannan dan kwangilar ya yi watsi da aikin ba tare da wani kwakkwaran dalili ba.
A cewar Leadrship, Dan majalisar ya ce,”Rashin kammala aikin ya yi mutukar shafar kokarin gwamnatin tarayya na aiwatar da tsarin ta na fadada tattalin arziki na bangaren ayyukan gona, domin bunkasa samar da abinci tare da wadata kasa da abincin”. Inji Dr Hamisu.