fidelitybank

A gaggauta kama masu haƙa ma’adanai bisa rushewar makaranta – Gwamnan Filato

Date:

Gwamna Caleb Mutfwang na jihar Filato a ranar Asabar ya ba da umarnin rufe makarantar Saint Academy da ke Busa Buji a karamar hukumar Jos ta Arewa cikin gaggawa.

Gwamnan ya kuma bayar da umarnin kame masu sana’ar hakar ma’adinai a kewayen mazauna jihar.

A ranar Juma’a ne wani bene mai hawa biyu ya ruguje a makarantar, inda ya yi sanadin mutuwar mutane sama da 20 da suka hada da dalibai da malamai, yayin da wasu da dama suka samu raunuka daban-daban.

Rundunar ‘yan sandan jihar ta bakin jami’in hulda da jama’a na rundunar, DSP Alfred Alabo, ta tabbatar da mutuwar mutane 22 tare da ceto wasu 132, daga cikinsu suna samun kulawa a wasu manyan cibiyoyin lafiya a babban birnin jihar.

Mutfwang ya bada umarnin ne a lokacin da ya ziyarci wurin da lamarin ya faru.

“Ina ba da umarnin rufe makarantar Saint Academy da gaggawa.

“Kuma ina kuma umarci jami’an tsaro da su kama duk wani mai aikin hako ma’adinai a yankunan da ke fadin jihar.”

Da yake jajantawa iyalan wadanda lamarin ya rutsa da su, gwamnan ya yi alkawarin cewa gwamnati za ta dauki nauyin kula da wadanda suka jikkata.

today daily post news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp