Majalisar wakilai ta yi kira da a kafa sansanin soji a yankin Bukuyum sakamakon ƙamarin matsalar tsaro a yankin.
Ɗanmajalisar da ke wakiltar yankin, Sulaiman Abubakar Gumi ne ya gabatar da ƙudirin buƙatar hakan, inda ya ce ƴanbindiga sun mayar da yankinsa matsayin mafaka.
Ya ce suna tserewa yankin ne sakamakon yaƙarsu da ake yi a yankin Shinkafi da kuma sulhun da gwamnatin Kaduna ta yi da su.
Sojojin ƙasar dai sun ce suna ci gaba da luguden wuta kan ƴanbindiga, kuma sun ce suna samu nasara.