Majalisar wakila ta buƙaci hukumar da ke kula da kamfanonin sadarwa ta ƙasar, NCC ta janye karin kuɗin kira da na data da kamfanonin sadarwar suka yi.
Karin kuɗin kiran na kashi 50 cikin 100 da Kamfanonin sadarwar suka yi ya soma aiki cikin makon nan.
Sai dai majalisar wakilan ta ce ƙari a wannan lokaci babu adalci saboda ƴanƙasar na cikin matsin rayuwa.
Hon. Umar Ajilo daga jihar Kaduna ya shaida wa BBC cewa majalisar ba za ta amince da wannan ƙarin ba.
”Duba da irin wannan yanayi da ƴanƙasa ke ciki na matsin rayuwa da rashin aikin yi da rashin abubuwan more rayuwa, ba yadda za a yi a yi musu ƙari, wannan bai kamata ba”, a cewar ɗan majalisar.
Ya ƙara da cewa bai ma kamata a yi ƙari ba la’akari da rashin kyawun sadarwar da ake fama da ita a ƙasar.
Ya ce majalisar wakilan ta buƙaci hukumar NCC ta zauna domin janye wannan mataki.
Hon Umar Ajilo ya ce idan abin ta ci tura majalisar ka iya gayyato jagororin hukumar NCC domin su zo su yi mata bayani kan dalilin ƙin janye matakin.