fidelitybank

A gaggauta janye karin kudin kira da na data a Najeriya – Majalisa

Date:

Majalisar wakila ta buƙaci hukumar da ke kula da kamfanonin sadarwa ta ƙasar, NCC ta janye karin kuɗin kira da na data da kamfanonin sadarwar suka yi.

Karin kuɗin kiran na kashi 50 cikin 100 da Kamfanonin sadarwar suka yi ya soma aiki cikin makon nan.

Sai dai majalisar wakilan ta ce ƙari a wannan lokaci babu adalci saboda ƴanƙasar na cikin matsin rayuwa.

Hon. Umar Ajilo daga jihar Kaduna ya shaida wa BBC cewa majalisar ba za ta amince da wannan ƙarin ba.

”Duba da irin wannan yanayi da ƴanƙasa ke ciki na matsin rayuwa da rashin aikin yi da rashin abubuwan more rayuwa, ba yadda za a yi a yi musu ƙari, wannan bai kamata ba”, a cewar ɗan majalisar.

Ya ƙara da cewa bai ma kamata a yi ƙari ba la’akari da rashin kyawun sadarwar da ake fama da ita a ƙasar.

Ya ce majalisar wakilan ta buƙaci hukumar NCC ta zauna domin janye wannan mataki.

Hon Umar Ajilo ya ce idan abin ta ci tura majalisar ka iya gayyato jagororin hukumar NCC domin su zo su yi mata bayani kan dalilin ƙin janye matakin.

vanguard newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...
X whatsapp