fidelitybank

A gaggauta gudanar da bincike akan harin da aka kaiwa motocin Tinubu – Gwamnan Legas

Date:

Gwamnan jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu, ya bayar da umarnin a gudanar da bincike kan harin da aka kai ranar Lahadi kan wata motar safa da ke jigilar ‘yan jarida a cikin ayarin motocin tsohon gwamnan Legas, kuma dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC a zaben 2023, Bola Ahmed Tinubu.

Lamarin ya faru ne tsakanin Ebute-Ero da Adeniji, Iga-Iduganran, a lokacin da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Tinubu ya ziyarci fadar Oba na Legas, Oba Rilwan Akiolu.

Gwamna Sanwo-Olu ya kuma ba da umarnin cewa dole ne a kamo wadanda ke da hannu a lamarin tare da hukunta su. Bayan haka. gwamnati za ta karbi kudin asibiti na wadanda suka jikkata a lamarin.

Ya ce: “Gwamnatin jihar Legas ta yi Allah wadai da lamarin. Muna mutunta kafafen yada labarai kuma gwamnati a kodayaushe tana tabbatar da cewa sun samar da yanayi mai kyau don gudanar da ayyukansu.”

“Ba za a bar kowa ko kungiya su lalata dangantakarmu da kafafen yada labarai ba. Legas ba ta da wurin ’yan iska.”

A ranar Lahadin da ta gabata ne aka tarbi Tinubu cikin jerin gwano da murna daga magoya bayansa.

legit latest news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dangote ya rage farashin litar mai zuwa ₦820

Kamfanin matatar man Dangote ya rage farashin litar mai...

Dubai ta sake tsaurara matakan bai wa ‘yan Najeriya biza

Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa, UAE ta sake sanya wasu dokoki...

‘Yan Bindigar Katsina ‘yan asalin jihar mu ne – Gwamna

Gwamnan Katsina Umaru Dikko Radda ya ce galibin 'yan...

Zan yi wa ADC aiki ina cikin jam’iyyar PDP – Sule Lamido

Jigo a babbar jam’iyyar hamayya ta PDP a Najeriya...

Buhari da Tinubu kan su a hade ya ke – Garba Shehu

Mai magana da yawun tsohon Shugaban kasa, Muhammadu Buhari...

Ganduje ya kama aiki a hukumar kula da filayen jirgin sama

Tsohon shugaban jam'iyyar APC mai mulki, Abdullahi Ganduje, ya...

JAMB ta amince da maki 150 mafi ƙanƙanta don samun gurbin karatu a jami’o’i

Hukumar shirya jarrabawar shiga Jami'o'i ta Najeriya (JAMB) ta...

ASUU ta dakatar da yajin aikin da ta fara

Ƙungiyar Malaman Jami'o'i ta Najeriya, ASUU da dakatar yajin...

Masu haɗakar ADC na ɓaɓatu ne saboda rashin gwamnati – Radda

Gwamnan jihar Katsina, Mallam Dikko Umar Radda ya yi...

Ba ruwan Biri da gada a makamin Nukiliya – Shettima

Mataimakin shugaba Najeriya Kashim Shettima ya ce ƙasar za...

An kashe Mutane 70 a jihar Filato

Rahotonni daga jihar Filato na cewa ƴanbindiga sun kai...

Ambaliya ta kashe mutane 100 a Amurka

Hukumomi a jihar Tesxas da ke Amurka sun bayyana...
X whatsapp