fidelitybank

A gaggauta gudanar da bincike akan harin da aka kaiwa motocin Tinubu – Gwamnan Legas

Date:

Gwamnan jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu, ya bayar da umarnin a gudanar da bincike kan harin da aka kai ranar Lahadi kan wata motar safa da ke jigilar ‘yan jarida a cikin ayarin motocin tsohon gwamnan Legas, kuma dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC a zaben 2023, Bola Ahmed Tinubu.

Lamarin ya faru ne tsakanin Ebute-Ero da Adeniji, Iga-Iduganran, a lokacin da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Tinubu ya ziyarci fadar Oba na Legas, Oba Rilwan Akiolu.

Gwamna Sanwo-Olu ya kuma ba da umarnin cewa dole ne a kamo wadanda ke da hannu a lamarin tare da hukunta su. Bayan haka. gwamnati za ta karbi kudin asibiti na wadanda suka jikkata a lamarin.

Ya ce: “Gwamnatin jihar Legas ta yi Allah wadai da lamarin. Muna mutunta kafafen yada labarai kuma gwamnati a kodayaushe tana tabbatar da cewa sun samar da yanayi mai kyau don gudanar da ayyukansu.”

“Ba za a bar kowa ko kungiya su lalata dangantakarmu da kafafen yada labarai ba. Legas ba ta da wurin ’yan iska.”

A ranar Lahadin da ta gabata ne aka tarbi Tinubu cikin jerin gwano da murna daga magoya bayansa.

vanguard (nigeria)

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp