Tsohon shugaban jam’iyyar PDP na jihar Oyo, Hafeez Tijani Adiaro ya rasu.
Marigayin ya jajirce a fagen siyasa a zamanin gwamnatin tsohon Gwamna, Rasheed Ladoja na jihar Oyo.
Wasu majiyoyin da su ka zanta da POLITCAL NIGERIA a ranar Talata sun ce babban dan siyasar Oke-Ogun ya mutu ranar Litinin.
A halin yanzu, ba za a iya tantance shekarunsa da ainihin dalilin mutuwar Adiaro ba, har zuwa lokacin fitar da wannan rahoto.