fidelitybank

A faɗa duban sabon Wata a ranar Addabar – Sarkin Musulmi

Date:

Sarkin Musulmin Najeriya, Muhammad Sa’ad Abubakar, wanda shi ne shugaban Majalisar ƙoli ta addinin Musulunci a ƙasar ya buƙaci al’umma su duba jinjirin watan Shawwal na shekarar Musulunci ta 1446 (Bayan Hijira) a gobe Asabar.

Hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da fadar Sarkin Musulmin ta fitar a yau Juma’a, wadda ta samu sa hannun shugaban kwamitin da ke bai wa sarkin Musulmi shawara kan harkokin addinin Musulunci, Farfesa Sambo Wali Junaidu.

Sanarwar ta ce “Ana sanar da Musulmai cewa Asabar, 29 ga watan Maris, 2025, wadda ta yi daidai da 29 ga watan Ramadan, ita ce ranar da za a yi duban jinjirin watan Shawwal na shekarar 1446 (Bayan Hijira).

“Saboda haka ana buƙatar Musulmai su dubi watan a ranar Asabar, sannan idan sun gani su kai rahoto ga hakimi ko dagacin yankinsu, wanda shi kuma zai isar da saƙon ga Sarkin Musulmi, Sa’ad Abubakar.”

Ganin jinjirin watan Shawwal ne zai tabbatar da ƙarshen azumin Ramadan, inda za a gudanar da sallar Eid el-Fitr a ranar ɗaya ga watan na Shawwal.

Idan aka ga jinjirin watan a ranar Asabar, hakan na nufin za a yi hawan sallah ƙarama a ranar Lahadi bayan yin azumi 29, sai dai idan aka gaza ganin watan, Sarkin Musulmin – bisa al’ada – zai bayar da sanarwar cike azumi 30 kamar yadda addinin Musulunci ya tanada.

nnn.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp