Sarkin Musulmi kuma Shugaban Majalisar Koli ta Harkokin Addinin Musulunci ta ƙasa, Sa’ad Abubakar, ya umarci Musulmi da su duba jinjirin watan Shawwal na shekarar 1444 bayan hijira daga ranar Alhamis.
Abubakar ya yi wannan kiran ne a cikin wata sanarwa a ranar Laraba mai dauke da sa hannun Farfesa Sambo Junaidu, shugaban kwamitin ba da shawara kan harkokin addini na Majalisar Sarkin Musulmi.
“Ana sanar da al’ummar musulmi cewa ranar Alhamis 20 ga watan Afrilu, daidai da 29 ga watan Ramadan 1444, ita ce ranar neman jinjirin watan Shawwal 1444.
“Saboda haka an bukaci musulmi da su fara neman jinjirin watan Shawwal na shekara ta 1444 a ranar Alhamis, kuma su kai rahoto ga Hakimin Kauye mafi kusa da su domin su samu damar tattaunawa da Sarkin Musulmi,” in ji Junaidu.
Sarkin Musulmi ya yi addu’ar Allah ya taimaki Musulmi wajen gudanar da ayyukansu na addini.
Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya ya bayar da rahoton cewa ganin jinjirin wata zai nuna cewa an kawo karshen azumin farilla na wata guda da musulmi ke yi a fadin Najeriya.
Shawwal shine wata na 10 a musulunci.