fidelitybank

A faɗa duban sabon Wata a ranar Addabar – Sarkin Musulmi

Date:

Sarkin Musulmin Najeriya, Muhammad Sa’ad Abubakar, wanda shi ne shugaban Majalisar ƙoli ta addinin Musulunci a ƙasar ya buƙaci al’umma su duba jinjirin watan Shawwal na shekarar Musulunci ta 1446 (Bayan Hijira) a gobe Asabar.

Hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da fadar Sarkin Musulmin ta fitar a yau Juma’a, wadda ta samu sa hannun shugaban kwamitin da ke bai wa sarkin Musulmi shawara kan harkokin addinin Musulunci, Farfesa Sambo Wali Junaidu.

Sanarwar ta ce “Ana sanar da Musulmai cewa Asabar, 29 ga watan Maris, 2025, wadda ta yi daidai da 29 ga watan Ramadan, ita ce ranar da za a yi duban jinjirin watan Shawwal na shekarar 1446 (Bayan Hijira).

“Saboda haka ana buƙatar Musulmai su dubi watan a ranar Asabar, sannan idan sun gani su kai rahoto ga hakimi ko dagacin yankinsu, wanda shi kuma zai isar da saƙon ga Sarkin Musulmi, Sa’ad Abubakar.”

Ganin jinjirin watan Shawwal ne zai tabbatar da ƙarshen azumin Ramadan, inda za a gudanar da sallar Eid el-Fitr a ranar ɗaya ga watan na Shawwal.

Idan aka ga jinjirin watan a ranar Asabar, hakan na nufin za a yi hawan sallah ƙarama a ranar Lahadi bayan yin azumi 29, sai dai idan aka gaza ganin watan, Sarkin Musulmin – bisa al’ada – zai bayar da sanarwar cike azumi 30 kamar yadda addinin Musulunci ya tanada.

daily post nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp