fidelitybank

A Daura za a yi jana’izar Buhari – Radda

Date:

Gwamnan Katsina Dikko Umaru Radda ya ce iyalan Muhammadu Buhari sun yanke shawarar yi masa jana’iza a garin Daura mahaifarsa da ke jihar ta Katsina.

Da yake magana da kafar yaɗa labarai ta DW Hausa, Dikko Radda ya ce yana birnin na Landan ya samu labarin rasuwar inda ya je duba shi.

“Na zo ranar Juma’a domin duba shi, muna shirin dawowa gida kuma sai ga labarin rasuwar tasa,” in ji shi.

“Yanzu muka rabu da iyalansa a asibitin da ya rasu kuma an yi ittifaƙi za a kai shi gida Daura a jihar Katsina domin yi masa sutura. Insha Allau za su baro Ingila da safe.

“Muna sa ran gobe Litinin za a yi jana’izar tasa saboda muna sa ran mataimakin shugaban ƙasa zai iso Ingila cikin dare, su taho da mamaci da safe.”

Fadar shugaban Najeriya ta ce Bola Tinubu ya umarci mataimakinsa Kashim Shettima ya je Landan domin raka gawar Buhari zuwa gida Najeriya.

nigerianewspapers.com.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp