Jigo a jam’iyar APC, Dr Salihu Lukman, ya yi kira da a kakabawa shugabannin jam’iyyar da ke kokarin kawo cikas ga babban taron kasa da aka shirya gudanarwa a ranar 26 ga watan Fabrairu.
Lukman, tsohon darekta janar na kungiyar gwamnonin ci gaba (PGF), kungiyar gwamnonin da aka zaba a karkashin jam’iyyar APC, ya yi wannan kiran ne a wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi, a Abuja.
A cewarsa, yakin neman dawo da jam’iyyar zuwa ga manufar kafa jam’iyyar, dole ne ya kasance da kakkausar murya da kuma fadin albarkacin bakinsa a babban taronta na kasa mai zuwa, inda ake sa ran za a zabi sabbin shugabannin jam’iyyar na kasa da za su tafiyar da harkokin jam’iyyar.
“A sanya takunkumi ga duk wani shugaba da ya ke kawo tsaiko yayin taron jam’iyar,” in ji Lukman.
Ya yi nuni da cewa rigingimun da ke faruwa a cikin jam’iyyar na ruguza ta bisa tsari, domin haka dole ne a dakatar da su kafin lamarin ya yi muni.