Shugaban Faransa, Emmanuel Macron ya yi kira da a dakatar da yaƙi don ayyukan jin ƙai ga yakin Gaza.
Macro yayi wannan kira ne yayin wani taron ƙasashen duniya da aka shirya a birnin Paris
Ƙasashen G7 wanda suka haɗa da Faransa su ma sun yi wannan kiran a jiya, a wani taron ministocin harkokin kasashe waje a Tokyo.
Macron ya kuma ce taimakon da Faransa ke bai wa Falasɗinawa zai ƙaru sau biyar a shekara mai zuwa, daga Yuro miliyan 20 a bana zuwa Yuro miliyan 100 a shekarar 2024.