Tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo, ya ce bai dace a zargi kabilar Igbo kadai da yunkurin ballewa daga Najeriya ba.
Wannan dai shi ne kamar yadda tsohon shugaban na Najeriya ya ce manyan kabilun kasar uku a lokaci guda sun yi yunkurin wargaza al’ummar kasar ta hanyar ballewa.
Ya ce yakan ji bacin rai a duk lokacin da ya ji wasu na cewa babu wani dan kabilar Ibo da zai zama Shugaban Najeriya saboda yadda ‘yan kabilar suka shiga cikin wani kazamin juyin mulkin da aka yi a ranar 15 ga watan Janairun 1966 wanda ya ruguza jamhuriya ta farko.
Obasanjo ya bayyana cewa akwai ‘yan Najeriya daga wasu sassan kasar da su ma suka yi yunkurin ballewa daga Najeriya.
Ya bayyana haka ne a lokacin da yake jawabi ga tawagar mutane 20 na kungiyar League of Northern Democrats karkashin jagorancin tsohon gwamnan jihar Kano, Ibrahim Shekarau, a dakin karatu na Olusegun Obasanjo da ke Abeokuta, babban birnin jihar Ogun.
Dattijon ya tuna cewa akwai wani yunkuri mai karfi da Arewa ta yi na ficewa daga Najeriya ta hanyar abin da ya kira motar Araba.
“Ina ganin dukkanmu a Najeriya dole ne mu sake tunani… Yana zubar min da zuciya yayin da mutane ke cewa saboda Igbo sun yi ballewa, dan kabilar Igbo ba zai iya zama shugaban Najeriya ba.
“Nace wace banza ce? Babu wani yanki na Najeriya da bai shirya ballewa ba. Menene ‘Araba’ a Arewa? Arewa ta shirya wargaza Najeriya. Ahmed Jooda, babban abokina, ya ce.
“Mene ne laifin cin amanar kasa? To, a cikinmu wa zai iya cewa na fi wancan? Babu! Don haka, mu hada kawunanmu waje guda, mu gina kasa tare,” inji shi.
Obasanjo ya yi nuni da cewa ‘yan Najeriya da dama sun yi na’am da damuwar da kungiyar ‘yan jam’iyyar Democrat ta kasa ta bayyana. Tsohon shugaban kasar ya ce zai marawa kungiyar baya idan ta kasance mai kishin kasa maimakon na larduna ko yankin da ake da su a yanzu.