fidelitybank

A daina zargin ƙabilar Inyamurai da yunƙurin ɓallewa daga Najeriya – Obasanjo

Date:

Tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo, ya ce bai dace a zargi kabilar Igbo kadai da yunkurin ballewa daga Najeriya ba.

Wannan dai shi ne kamar yadda tsohon shugaban na Najeriya ya ce manyan kabilun kasar uku a lokaci guda sun yi yunkurin wargaza al’ummar kasar ta hanyar ballewa.

Ya ce yakan ji bacin rai a duk lokacin da ya ji wasu na cewa babu wani dan kabilar Ibo da zai zama Shugaban Najeriya saboda yadda ‘yan kabilar suka shiga cikin wani kazamin juyin mulkin da aka yi a ranar 15 ga watan Janairun 1966 wanda ya ruguza jamhuriya ta farko.

Obasanjo ya bayyana cewa akwai ‘yan Najeriya daga wasu sassan kasar da su ma suka yi yunkurin ballewa daga Najeriya.

Ya bayyana haka ne a lokacin da yake jawabi ga tawagar mutane 20 na kungiyar League of Northern Democrats karkashin jagorancin tsohon gwamnan jihar Kano, Ibrahim Shekarau, a dakin karatu na Olusegun Obasanjo da ke Abeokuta, babban birnin jihar Ogun.

Dattijon ya tuna cewa akwai wani yunkuri mai karfi da Arewa ta yi na ficewa daga Najeriya ta hanyar abin da ya kira motar Araba.

“Ina ganin dukkanmu a Najeriya dole ne mu sake tunani… Yana zubar min da zuciya yayin da mutane ke cewa saboda Igbo sun yi ballewa, dan kabilar Igbo ba zai iya zama shugaban Najeriya ba.

“Nace wace banza ce? Babu wani yanki na Najeriya da bai shirya ballewa ba. Menene ‘Araba’ a Arewa? Arewa ta shirya wargaza Najeriya. Ahmed Jooda, babban abokina, ya ce.

“Mene ne laifin cin amanar kasa? To, a cikinmu wa zai iya cewa na fi wancan? Babu! Don haka, mu hada kawunanmu waje guda, mu gina kasa tare,” inji shi.

Obasanjo ya yi nuni da cewa ‘yan Najeriya da dama sun yi na’am da damuwar da kungiyar ‘yan jam’iyyar Democrat ta kasa ta bayyana. Tsohon shugaban kasar ya ce zai marawa kungiyar baya idan ta kasance mai kishin kasa maimakon na larduna ko yankin da ake da su a yanzu.

www.legit.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp