fidelitybank

A daina zargin ƙabilar Inyamurai da yunƙurin ɓallewa daga Najeriya – Obasanjo

Date:

Tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo, ya ce bai dace a zargi kabilar Igbo kadai da yunkurin ballewa daga Najeriya ba.

Wannan dai shi ne kamar yadda tsohon shugaban na Najeriya ya ce manyan kabilun kasar uku a lokaci guda sun yi yunkurin wargaza al’ummar kasar ta hanyar ballewa.

Ya ce yakan ji bacin rai a duk lokacin da ya ji wasu na cewa babu wani dan kabilar Ibo da zai zama Shugaban Najeriya saboda yadda ‘yan kabilar suka shiga cikin wani kazamin juyin mulkin da aka yi a ranar 15 ga watan Janairun 1966 wanda ya ruguza jamhuriya ta farko.

Obasanjo ya bayyana cewa akwai ‘yan Najeriya daga wasu sassan kasar da su ma suka yi yunkurin ballewa daga Najeriya.

Ya bayyana haka ne a lokacin da yake jawabi ga tawagar mutane 20 na kungiyar League of Northern Democrats karkashin jagorancin tsohon gwamnan jihar Kano, Ibrahim Shekarau, a dakin karatu na Olusegun Obasanjo da ke Abeokuta, babban birnin jihar Ogun.

Dattijon ya tuna cewa akwai wani yunkuri mai karfi da Arewa ta yi na ficewa daga Najeriya ta hanyar abin da ya kira motar Araba.

“Ina ganin dukkanmu a Najeriya dole ne mu sake tunani… Yana zubar min da zuciya yayin da mutane ke cewa saboda Igbo sun yi ballewa, dan kabilar Igbo ba zai iya zama shugaban Najeriya ba.

“Nace wace banza ce? Babu wani yanki na Najeriya da bai shirya ballewa ba. Menene ‘Araba’ a Arewa? Arewa ta shirya wargaza Najeriya. Ahmed Jooda, babban abokina, ya ce.

“Mene ne laifin cin amanar kasa? To, a cikinmu wa zai iya cewa na fi wancan? Babu! Don haka, mu hada kawunanmu waje guda, mu gina kasa tare,” inji shi.

Obasanjo ya yi nuni da cewa ‘yan Najeriya da dama sun yi na’am da damuwar da kungiyar ‘yan jam’iyyar Democrat ta kasa ta bayyana. Tsohon shugaban kasar ya ce zai marawa kungiyar baya idan ta kasance mai kishin kasa maimakon na larduna ko yankin da ake da su a yanzu.

vgn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Bayan hutun Sallah Tinubu zai koma Abuja

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu na kan hanyarsa ta komawa...

Mutane 570 aka kashe a Najeriya cikin watan Afrilu – Rahoto

Hukumar kare haƙƙin ɗan'adam a Najeriya ta ce, adadin...

PDP ba za ta mutu ba duk da rikicin cikin gida – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya ce...

Sojoji sun kashe riƙaƙen ɗan bindiga Guddel a Kaduna

Sojoji sun yi nasarar kawar da fitaccen shugaban ‘yan...

Fadar shugaban ƙasa ta yi kakkausar gargaɗi a kan Ndume

Fadar shugaban kasa ta yi kakkausar gargadi ga dan...

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...
X whatsapp