fidelitybank

A daina nuna wariya ga yara masu nakasa a makarantun gwamnati – Ministan Ilimi

Date:

Karamin Ministan Ilimi, Yusuf Sununu, ya yi kira da a daina nuna wariya ga yara masu nakasa a makarantun gwamnati a fadin kasar nan.

Sununu ya yi wannan bukata ne a wajen taron tunawa da ranar nakasassu ta duniya ta 2023 da aka gudanar a Abuja.

Ministan wanda Dr Clarence Ujam na ma’aikatar ilimi ya wakilta, ya ce binciken ya nuna cewa ana kin yara masu nakasa a makarantun gwamnati saboda rashin kayan aiki da masu kula da su, lamarin da ya ke son duk masu ruwa da tsaki su hada hannu su daina.

“Bincike ya nuna cewa yara masu nakasa ana watsi da su daga makarantun gwamnati saboda rashin kayan aiki da masu kula da su. Dole ne a dakatar da wannan nuna wariya ta hanyar hadin gwiwa na dukkan masu ruwa da tsaki,” inji shi.

Ya ce kuma abin takaici ne yadda yara masu nakasa, baya ga ilimi, ana tauye musu hakkinsu da dama, ciki har da munanan hasashe.

Don haka ya yi kira da a aiwatar da kudurin ci gaba mai dorewa mai lamba 4, wanda ke bukatar hada kai da bunkasa damammaki ga nakasassu.

nnnhausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp