Wasu mazauna jihar Zamfara sun yi ikirarin cewa, ba za su iya gudanar da bukukuwan sallar Eid-el-Kabir na bana a gidajensu ba, saboda ‘yan bindiga ne ke kula da yawancin al’umomin jihar.
Naija News ta ba da rahoton cewa, Musulmi a duk faɗin duniya sun yi bikin Eid-el-Kabir na bana wanda aka fi sani da Eid al-Adha a ranar Asabar, 9 ga Yuli, 2022.
Sai dai a yayin da da dama ke gudanar da bukukuwa a gidajensu, mazauna karkara sun ce gidajensu ba su da tsaro don haka ba za su iya yin bukukuwan Sallar Eid-el-Kabir ba.
Wasu daga cikin mutanen yankin da suka zanta da Daily Post a Gusau babban birnin jihar, sun bayyana albashi da alawus-alawus da ake biyan jami’an tsaro a matsayin babban asara.
Sun ce, hukumomin tsaro sun gaza shawo kan matsalar tsaro a jihar. Al’ummar yankin sun koka da cewa duk da irin tabbacin da jami’an tsaro suka ba su na samar da isasshen tsaro, sun kasa gudanar da bukukuwan Sallar Kabir saboda rashin tsaro.
A cewar wani Umar Magami, galibin mutanen kauyen sun gudanar da bukukuwan Sallah a Gusau da sauran garuruwa saboda babu wata al’umma da ke da tsaro a jihar Zamfara.