Mutum shida ne suka ji mummunan rauni a hatsarin da wani jirgi mai saukar Ungulu a mallakin rundunar ƴan sandan Najeriya ya yi a Bauchi a jiya Laraba.
Gidan rediyon gwamnatin tarayya ya rawaito Hcewa ukumar Bincike Haɗurra ta ƙasa, AIB ta tabbatar da labarain.
Sai dai a sanarwar da hukumar AIB ta fitar ta ce babu wanda ya mutu a hatsarin.
Hukumar ta ce Hukumar Kula da Sararin Samaniyar Najeriya NAMA ce ta sanar da ita faruwar lamarin kuma tuni an fara bincike.
Hukumar ta nemi duk wanda lamarin ya faru a kan idonsa ko ya naɗi wani bayani na faruwarsa da ya kai mata, domin taimaka wa wajen binciken da ake yi.
AIB ta kuma buƙci jama’a da ƴan jarida da su tsare sirrin waɗanda hatsarin ya rutsa da su ta hanyar dakatar da yaɗa jita-jita kan abin da ya haddasa hatsarin har sai an fitar da bayani a hukumance. A cewar BBC