Babban Sakataren Majalisar Ɗinkin Duniya, Antonio Guterres, ya yi kira ga mahukunta a Najeriya su bincika zargin tilasta zubar da ciki da aka ce rundunar sojan ƙasar na yi a yankin arewa maso gabashin ƙasar.
A ranar Laraba ne kamfanin labarai na Reuters ya ruwaito cewa Rundunar Sojan Najeriya ta shafe shekara tara tana gudanar da wani shirin zubar wa da mata ciki waɗanda ‘yan Boko Haram suka yi wa fyaɗe ta hanyar tilasta musu.
Rahoton ya yi iƙirarin cewa an zubar da ciki aƙalla 10,000 na matan da Boko Haram suka sace tare da mayar da su matansu tun daga 2013.
“Babban Sakataren ya nuna damuwa game da zargin zubar wa da mata ciki…kuma ya nemi a gudanar da cikakken bincike tare da ɗaukar matakan gyara,” a cewar mai magana da yawunsa Stephane Dujarric cikin saƙon da ya aike wa Reuters.
Tuni rundunar sojan ta musanta zargin, tana mai kiran rahoton na Reuters a matsayin “ɓata suna”.