Tsohon dan majalisar dokoki ta kasa, Shehu Sani, ya dage cewa a bar ‘yan Najeriya su zabi shugabansu.
Bayanin hakan na kunshe ne a wani sako da ya fitar ta shafin sa na Twitter da aka tabbatar a ranar Alhamis.
Jawabin nasa ya biyo bayan jawabin da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya yi wa ‘yan Najeriya kan manufar sake fasalin Naira.
Karanta Wannan: A cigaba da karbar tsohuwar Dari Biyu amma kar a karbi sauran – Buhari
Buhari ya bayar da umarnin a dawo da darajar Naira 200 a kasuwanni.
Shugaban ya kuma ce manufar sake fasalin Naira zai taimaka wajen dakile sayen kuri’u a zabe mai zuwa.
Sani, ya yarda da Buhari, ya ce kada a siya ko sayar da mulkin siyasa.
Ya wallafa a shafinsa na twitter cewa, “Ya kamata shugaban Najeriyar na gaba ya fito ta hanyar kada kuri’a ba tsarin takara ba. Bai kamata a siya ko sayar da ikon siyasa ba.
“Raba kudi ga masu zabe don kada kuri’a ba dimokuradiyya ba ne; wannan ne lokacin da za a kawo karshensa.”