Gomman masu zanga-zanga ne suka taru a birnin Legas da ke kudancin Najeriya don nuna goyon bayansu ga al’ummar Falasɗinu.
Mutanen maza da mata sun fito ne a yau Asabar ɗauke da kwalaye iri-iri da ke neman “adalci ga Falasɗinu” da kuma “a bai wa Falasɗinu ‘yanci”.
Da yawan waɗanda suka yi magana a wurin taron sun yi kira ga gwamnatin Najeriya ta ƙaurace wa hulɗa da Isra’ila, wadda ta ƙaddamar da hare-hare kan Zirin Gaza bayan mayaƙan Hamas sun kai mata hari.