fidelitybank

An ceto Mutane 26 da kwale-kwale ya kife da su a Sokoto

Date:

An samu nasarar ceto mutum 29 bayan hatsarin kwale-kwale da ya afku a jihar Sokoto, a cewar ɗan majalisar wakilai daga mazaɓar Goronyo/Gada na jihar, Bashir Gorau.

Ya ce ana fargabar akwai mutum 40 da suka ɓace kawo yanzu bayan da kwale-kwalen ɗauke da fasinjoji sama da 50 ya kife ranar Lahadi.

“Zuwa yanzu muna ci gaba da bibiyar lamarin, sannan akwai mutanen mu da suka iya ruwa da ke ƙoƙari wajen ganin sun cigaba da ceto sauran mutane. Mun ceto mutum 26 kawo yanzu,” kamar yadda ɗan majalisar ya shaida wa gidan talabijin na Channels a wata tattauna ranar Talata.

Ya kuma ce sun buƙaci hukumomin da ke kula da madatsar ruwa ta Goronyo da su rufe ruwan na tsawon kwanaki biyu don ganin ruwan ya ragu, saboda a ci gaba da aikin ceto.

Alkaluma da hukumar ba da agajin gaggawa ta ƙasa NEMA ta fitar tun da farko, sun nuna cewa ana fargabar kusan mutum 40 ne suka rasu a hatsarin.

Sai dai, Gorau ya yi imanin cewa “babu ainihin alkaluman waɗanda suka ɓace” daga wannan mummunan hatsari.

“Hasashe ne ake yi cewa mutum 40 ko 50 sun ɓace, sai dai babu takamaimen alkaluman mutanen,” in ji ɗan majalisar.

Ya kuma koka kan yadda ake yawan samun hatsarin jiragen ruwa, inda ya ɗora laifin hakan kan rashin bn matakan kariya na shiga ruwa.

legit.ng.news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp