fidelitybank

Emefiele na fuskantar tuhume-tuhume 14 a kotu

Date:

Tsohon gwamnan babban bankin Najeriya, Godwin Emefiele na fuskantar karin tuhume-tuhume 14, yayin da masu shigar da kara a Najeriya ke kara tsananta shari’ar da aka fara a watan Yunin da ya gabata bayan rantsar da shugaban kasa Bola Tinubu.

Lamarin ya sa an dakatar da Emefiele tare da korarsa daga aiki watanni hudu da suka gabata.

A watan Nuwamba ne dai Hukumar Yaƙi da cin Hanci da Rashawa (EFCC) ta fara tuhumar Emefiele da laifuka shida da suka haɗa da zamba da suka kai Naira biliyan 1.2.

Yayin da aka ci gaba da shari’ar a babbar kotu birnin tarayya Abuja, a ranar Alhamis, lauyan hukumar EFCC, Rotimi Oyedepo, ya ce an gyara tuhume-tuhumen da suka hada da na jabu, da laifin karya amana, samu ta hanyar karya da kuma bayar da cin hanci da rashawa.

Sabbin tuhume-tuhumen na zuwa ne bayan rahoton da wata tawagar shugaban kasa ta kafa domin gudanar da bincike a kan zargin aikata ba daidai ba a babban bankin kasar.

Lauyan Emefiele, Matthew Burkaa, ya bukaci lokaci domin duba sabbin tuhume-tuhumen kafin shigar da kara.

Duk da cewa an bayar da belinsa a watan Disamba, tare da takaita zirga-zirgarsa a babban birnin kasar, Abuja kaɗai.

Amma, a zaman da aka yi na ranar Alhamis, an gyara wadannan takunkumin, kuma a yanzu yana iya tafiya ko’ina cikin kasar.

naija hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp