fidelitybank

Da Ɗumi-Ɗumi: Ɗan marigayi Abacha ya rasu

Date:

Abdullahi Sani Abacha, daya daga cikin ‘ya’yan marigayi shugaban mulkin sojan Najeriya, Sani Abacha ya rasu.

Majiyar ‘yan uwa ta tabbatar da rasuwar Abdullahi ga POLITICS NIGERIA a ranar Asabar, inda suka ce,  an wayi gari a gidan danginsa na Nelson Mandela Street Abuja , ya rasu bayan ya kwanta bacci.

“Ya kasance cikin farin ciki da jin dadi a daren jiya amma an same gawarsa a safiyar yau. Ya rasu cikin kwanciyar hankali a cikin barcinsa,” wata majiya ta ce.

Dan uwansa, Mahmud Abacha, dan na hudu ga marigayi Abacha, shi ma ya tabbatar da wannan labari mai ban tausayi a wani sako da ya wallafa.

“Na rasa dan uwana Abdullahi. Allah ya jikansa da rahama a Jannatil Firdaus,” inji shi.

Jaridar ta tattaro cewa za a gudanar da sallar jana’izar da misalin karfe 4 na yamma a babban masallacin kasa dake Abuja a yammacin yau (Asabar).

An haife shi a shekarar 1987, marigayin yana daya daga cikin ‘ya’ya 10 da marigayi shugaban soji ya bari.

tribune

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...
X whatsapp