Jamiāan tsaro sun sami nasarar tsawo matsalar da ‘yan ta’adda suka tsare jirgin kasan da ya taso daga Abuja da ke kan hanyar Kaduna.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da kwamishinan tsaro na cikin gida da harkokin cikin gida Samuel Aruwan ya fitar a daren ranar Litinin.
Ya ce, gwamnatin jihar Kaduna ta samu rahotanni da dama na harin da aka kai kan hanyar jirgin kasa daga Abuja zuwa Kaduna a kewayen babban yankin Kateri-Rijana.
āAn tuntubi hukumomin da abin ya shafa cikin gaggawa, kuma an yi gaggawar tura jamiāai masu karfi zuwa yankin domin kare fasinjojin da ke cikin jirgin.
āAna ci gaba da kokarin isar da fasinjojin daga wurin da kuma sauran wadanda suka samu raunuka an garzaya da su asibiti domin samun kulawar gaggawa.
āGwamnatin jihar Kaduna za ta hada gwiwa da hukumar kula da sufurin jiragen kasa ta Najeriya (NRC) don tantance jerin sunayen fasinjojin da ke dauke da su domin bin diddigin sahihancin.