‘Yan bindiga sun kai farmaki mabanbanta a kauyukan ‘Yar Katsina, Nasarawar Mai Fara da Nasarawa duk a Zamfara, inda suka kashe mutum 33.
An gano cewa, Ada Aleru, gagararren shugaban ‘yan bindiga ne ya saka wa jama’a harajin Naira miliyan 40, amma suka gaza biya a yayin da ‘yan ta’addan suka shiga kauyen ‘Yar Katsina, suka tarar a na sallar Juma’a, amma suka hargitsa jama’a tare da halaka babban limamin.
‘Yan bindiga sun halaka sama da rayuka talatin, sun kuma yi garkuwa da wasu mata a hari mabanbanta a ranar Juma’a duka a jihar Zamfara,].
Daily Trust ta rawaito cewa, yankunan da aka kai farmakin sun hada da Nasarawar mai Fara da ke karamar hukumar Tsafe, ‘Yar Katsina a karamar hukumar Bungudu da kauyen Nasarawa da ka karamar hukumar Bakura.