fidelitybank

HISBA ta kamo masu siyar da Shisha a Kano

Date:

Hukumar Hisba ta Jihar Kano, ta kai sumame shagunan da ake sayar da Shisha a kan titin Bompai da ke jihar Kano, inda ta samu nasarar kama masu shagunan dake siyar da Shisha.

Wannan dai shi ne karo na farko da gwamnati ta fara aiwatar da dokar a faɗin jihar, tun bayan da majalisar dokoki ta sanyawa ƙudurin dokar hannu akan sha da siyar da Shisha.

Sashi na 13(7) na dokar sisha, wacce a ka sanyawa hannu a ranar 15 ga watan Nuwamba, 2021, ya ce sha da ta’ammali da shisha haramun ne a Jihar Kano.

Tuni dai hukumar ta fara kama masu sayar da shisha a jihar, inda su ma su ka ce duk da an hana, har yanzu ana kawo musu ita da ga kasashen Dubai da China.

Haka kuma sun yi ƙorafin cewa an fara aiwatar da dokar ne ba tare da an basu wa’adi ba.

Sun kuma ƙara da cewa ya kamata a ce an wayar musu da kai da kuma sanarwa mai tsawo kafin a zo a fara kai musu farmaki a wajajen sana’ar su.

Sun ce su sun za ci dokar ta tsaya ne a wajen masu guraren shan shishar ba wai dillalin ta ba.

Da ya ke ganawa da manema labarai, Shugaban Hukumar Hisbah, Muhammad Harun Ibn-Sina, ya ce, sun fara sumamen ne domin haka ayyukan hukumar ya gada.

A cewar sa, sashe na 13(7) na dokar hana shisha ya tabbatar da cewa ta an haramta amfani da ita a jihar Kano, inda ya jadda ƙudurin hukumar Hisbah na ci gaba da hana sha da sayar da ita a faɗin jihar.

A ƙarshe ya kuma jaddada ƙudurin hukumar wajen yaƙi da baɗala da kuma umarni da kyawawan ayyuka a jihar.

breaking news in nigeria today punch

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar Æ´an Æ™asarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan ÆŠaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp