fidelitybank

HISBA ta kamo masu siyar da Shisha a Kano

Date:

Hukumar Hisba ta Jihar Kano, ta kai sumame shagunan da ake sayar da Shisha a kan titin Bompai da ke jihar Kano, inda ta samu nasarar kama masu shagunan dake siyar da Shisha.

Wannan dai shi ne karo na farko da gwamnati ta fara aiwatar da dokar a faɗin jihar, tun bayan da majalisar dokoki ta sanyawa ƙudurin dokar hannu akan sha da siyar da Shisha.

Sashi na 13(7) na dokar sisha, wacce a ka sanyawa hannu a ranar 15 ga watan Nuwamba, 2021, ya ce sha da ta’ammali da shisha haramun ne a Jihar Kano.

Tuni dai hukumar ta fara kama masu sayar da shisha a jihar, inda su ma su ka ce duk da an hana, har yanzu ana kawo musu ita da ga kasashen Dubai da China.

Haka kuma sun yi ƙorafin cewa an fara aiwatar da dokar ne ba tare da an basu wa’adi ba.

Sun kuma ƙara da cewa ya kamata a ce an wayar musu da kai da kuma sanarwa mai tsawo kafin a zo a fara kai musu farmaki a wajajen sana’ar su.

Sun ce su sun za ci dokar ta tsaya ne a wajen masu guraren shan shishar ba wai dillalin ta ba.

Da ya ke ganawa da manema labarai, Shugaban Hukumar Hisbah, Muhammad Harun Ibn-Sina, ya ce, sun fara sumamen ne domin haka ayyukan hukumar ya gada.

A cewar sa, sashe na 13(7) na dokar hana shisha ya tabbatar da cewa ta an haramta amfani da ita a jihar Kano, inda ya jadda ƙudurin hukumar Hisbah na ci gaba da hana sha da sayar da ita a faɗin jihar.

A ƙarshe ya kuma jaddada ƙudurin hukumar wajen yaƙi da baɗala da kuma umarni da kyawawan ayyuka a jihar.

latest nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Turji ya saki Mutane 32 bayan zaman sulhu

Shahararren shugaban ‘yan bindiga, Bello Turji, ya saki mutane...

ADC ta gargadi El’Rufa’i kan ruguza jam’iyyar

Shugaban jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) a jihar Kaduna,...

An gindayawa Thomas Partey sharudan beli

An gindaya sharuddan belin tsohon dan wasan tsakiya na...

Fursunoni 37 na jiran zartas musu da hukuncin kisa a Bauchi

Fursunoni 37 da aka yanke wa hukuncin kisa bisa...

Kwamitin sulhu na MDD zai gana kan makomar Æ´an Isra’ila da ke hannun Hamas

Kwamitin tsaro na Majalisar ÆŠinkin Duniya zai tattauna yau...

Sojoji sun kashe ‘yan Boko Haram 17 a Borno da Adamawa

Sojoji da ke aiki ƙarƙashin rundunar Operation Haɗin Kai...

Falana ya caccaki Tinubu kan salon tattalin arzikin Najeriya

Fitaccen lauyan nan mai kare haƙƙin bil adama, Femi...

Yahudawa sun yiwa Netanyahu tutsu kan mamaye Gaza

Ƴan'uwan Isra'ilawan da aka yi garkuwa da su a...

Cin zarafin Daliba ya sanya yin zanga-zanga a China

Zanga-zanga ta ɓarke a kudancin China sakamakon cin zarafin...

Tinubu ya baiwa ‘yan wasan kwallon kwando dala dubu 100 da filaye a Abuja

Gwamnatin Tarayya ta karrama kungiyar kwallon kwando ta mata...

‘Yan siyasa na kara matsin lamba Jonathan ya fito takara a 2027 – Bashir

Tsohon mai taimaka wa tsohon shugaban kasa kan harkokin...

Gwamnati ta karbi tawagar ‘yan wasan kwallon kwando D’Tigress

Tawagar ƴan wasan ƙwallon kwando mata ta Najeriya ta...
X whatsapp