Rundunar Ƴan Sandan Farin Kaya, DSS, ta gaiyace ɗaya daga cikin waɗanda su ka shirya zanga-zangar #NoMoreBloodShed, Zainab Nasir Ahmed a Jihar Kano.
An shirya zanga-zangar ne domin jawo hankalin gwamnatin tarayya a kan kashe-kashen da ke ta’azzara a Arewacin Nijeriya sakamakon kisan gillar da a ka yiwa matafiya su 42 a Sokoto.
Zainab ta tabbatarwa jaridar DAILY NIGERIAN cewa ta na kan hanyarta ta zuwa ofishin rundunar domin amsa kiran da a ka yi mata.
“Ni dai kawai sun kira ni sun ce a na son gani na a ofishin DSS sakamakon zanga-zangar lumana da mu ka yi yau.A yanzu haka ina kan hanya ta ta zuwa ofishin a matsayi na na mai bin doka,” Zainab ta shaidawa DAILY NIGERIAN.
A yau ne dai matasa su ka hau kan titunan wasu jihohin arewa domin zanga-zangar lumana a kan kashe-kashen da ke faruwa a Arewa.