fidelitybank

Date:

 

 

 

Fitacciyar jarumar fina-finan Hausa, Fati Muhammad ta dawo Kannywood, bayan shafe shekaru goma sha huɗu da daina sana’ar.

Dawowar Fati ta kasance tare da fatan alheri daga masoyanta da masoyan fina-finan Hausa.

Ta dawo ne a matsayin mai shirya fina-finai, kamar yadda wata gajeriyar sanarwa ta bayyana a shafin Facebook na ‘Kannywoodcelebrities’.

A ranar Talatar nan dai sabbin hotunan jarumar su ka karaɗe shafukan Sada Zumunta, musamman Facebook da instagram, wanda hakan ke nuni da cewa al’umma suna farin ciki da dawowarta harkar fina-finan Hausa.

A cikin hotunan, a kwai wanda a ka nuno Fatin a zaune kan wata kujera yayin da ake ɗaukar wani sabon fim, wanda za ta taka rawa a cikin sa.

A na tunanin cewa wannan shine shiri na farko bayan dawowarta harkar fina-finan Hausa.

Fati, ƴar asalin Jihar Adamawa, ta fara harkar fim tun tana ƙarama.

Fina-finan ta da su ka yi fice sun hada da Sangaya, Zarge, Marainiya, Mujadala, Kudiri, Tutar So, Garwashi, Tawakkali, Gasa, Abadan Da’iman, Zo mu Zauna, Tangarda, Hujja, Al’ajabi, Halacci, Samodara, Zumunci, Murmushin Alkawari, Gimbiya, Bakandamiya, Taskar Rayuwa, Babban Gari da dai sauransu.

legit.news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp