fidelitybank

Date:

 

 

 

Fitacciyar jarumar fina-finan Hausa, Fati Muhammad ta dawo Kannywood, bayan shafe shekaru goma sha huɗu da daina sana’ar.

Dawowar Fati ta kasance tare da fatan alheri daga masoyanta da masoyan fina-finan Hausa.

Ta dawo ne a matsayin mai shirya fina-finai, kamar yadda wata gajeriyar sanarwa ta bayyana a shafin Facebook na ‘Kannywoodcelebrities’.

A ranar Talatar nan dai sabbin hotunan jarumar su ka karaɗe shafukan Sada Zumunta, musamman Facebook da instagram, wanda hakan ke nuni da cewa al’umma suna farin ciki da dawowarta harkar fina-finan Hausa.

A cikin hotunan, a kwai wanda a ka nuno Fatin a zaune kan wata kujera yayin da ake ɗaukar wani sabon fim, wanda za ta taka rawa a cikin sa.

A na tunanin cewa wannan shine shiri na farko bayan dawowarta harkar fina-finan Hausa.

Fati, ƴar asalin Jihar Adamawa, ta fara harkar fim tun tana ƙarama.

Fina-finan ta da su ka yi fice sun hada da Sangaya, Zarge, Marainiya, Mujadala, Kudiri, Tutar So, Garwashi, Tawakkali, Gasa, Abadan Da’iman, Zo mu Zauna, Tangarda, Hujja, Al’ajabi, Halacci, Samodara, Zumunci, Murmushin Alkawari, Gimbiya, Bakandamiya, Taskar Rayuwa, Babban Gari da dai sauransu.

dailypostnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp