Gwamnan Jihar Sokoto Aminu Waziri Tambuwal ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar shugaban kasa a zaɓen 2023 ƙarƙashin jam’iyyar PDP.
Tsohon Kakakin Majalisar Wakilai ta kasa, Tambuwal ya bayyana hakan ne a Sokoto babban birnin jihar a ranar Litinin bayan kammala tuntuɓa da neman shawara.
Ya ce, bayan sauararar shugabannin jam’iyyar mata da matasa, game da kiran da suke yi na ya kamata ya tsaya takara a ƙarƙashin jam’iyyar PDP.
Aminu Waziri Tambuwal shi ne gwamna na biyu da ya bayyana sha’awarsa ta tsayawa takarar a PDP, bayan Gwamnan Bauchi Bala Mohammed.