Shugaban kwamitin shiyya na jam’iyyar PDP kuma gwamnan jihar Binuwai, Samuel Ortom ya jaddada kudirin kwamitin na samar da tsarin shiyya da ke nuna bambancin jam’iyyar.
Ortom ya bayyana hakan ne a ranar Talata yayin da yake magana a taron kwamitin shiyya na mutane 37 da aka yi karo na biyu a Abuja, inda ya kara da cewa, an kara wa’adinsa zuwa ranar 5 ga Afrilu domin ya yi nisa da cimma burinsa.
A cewarsa, ‘yan takarar shugaban kasa guda bakwai sun sayi fom din tsayawa takara, kuma nuna sha’awarsu domin neman tikitin takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP gabanin zaben fidda gwanin jam’iyyar da za a yi a ranakun 28 da 29 ga watan Mayun 2022.
Ya kara da cewa, jam’iyyar na fuskantar matsin lamba ta yadda za ta sanya jam’iyyar ta ware ofisoshinta na kasa ta yadda ba za ta iya jefa jam’iyyar cikin kasadar rarrabuwar kawuna da ‘yan takarar da suka fito daga shiyyoyin kasa-siyasa daban-daban.