Janar Yakubu Gowon, tsohon shugaban kasa a mulkin soja, ya ce, Najeriya ta cancanci shugaba a 2023 da kuma bayanta da zai kai ƙasar ga nasara.
Ya bayyana haka ne a ranar Juma’a a Abuja lokacin da jami’an kungiyar Progressive Consolidation Group suka kai masa ziyara a gidansa da ke Asokoro, Abuja.
Gowon ya jaddada cewa, duk da cewa ba shi da alaka da siyasa, amma ya yi imanin cewa, shugabanni da ‘yan kasa a kowane mataki ya zama wajibi su tabbatar da zaman lafiya, ci gaba da hadin kan kasa.
Ya kuma tabbatar da yakininsa cewa, komai girman makirci da yanayi, Allah zai yanke hukunci na karshe.
Gowon ya ce, domin amfanin kasar nan, dole ne dukkan ‘yan siyasa da mabiyansu su duba fiye da gwagwarmayar neman mukamai da kuma dorewar imani a Nijeriya.
Ya bukaci kafafen yada labarai da su kara kaimi wajen tabbatar da hadin kan kasa.
“Ku dore da fata, ku yi imani da Najeriya kuma ku yi imani da dalilin hadin kai da zaman lafiya,” in ji Gowon.
A baya dai shugabannin PCG sun yi wata ganawar sirri da tsohon shugaban kasar.