fidelitybank

2023: Najeriya na buƙatar jajirtaccen shugaba — Gowon

Date:

Janar Yakubu Gowon, tsohon shugaban kasa a mulkin soja, ya ce, Najeriya ta cancanci shugaba a 2023 da kuma bayanta da zai kai ƙasar ga nasara.

Ya bayyana haka ne a ranar Juma’a a Abuja lokacin da jami’an kungiyar Progressive Consolidation Group suka kai masa ziyara a gidansa da ke Asokoro, Abuja.

Gowon ya jaddada cewa, duk da cewa ba shi da alaka da siyasa, amma ya yi imanin cewa, shugabanni da ‘yan kasa a kowane mataki ya zama wajibi su tabbatar da zaman lafiya, ci gaba da hadin kan kasa.

Ya kuma tabbatar da yakininsa cewa, komai girman makirci da yanayi, Allah zai yanke hukunci na karshe.

Gowon ya ce, domin amfanin kasar nan, dole ne dukkan ‘yan siyasa da mabiyansu su duba fiye da gwagwarmayar neman mukamai da kuma dorewar imani a Nijeriya.

Ya bukaci kafafen yada labarai da su kara kaimi wajen tabbatar da hadin kan kasa.
“Ku dore da fata, ku yi imani da Najeriya kuma ku yi imani da dalilin hadin kai da zaman lafiya,” in ji Gowon.

A baya dai shugabannin PCG sun yi wata ganawar sirri da tsohon shugaban kasar.

legit.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp