Kungiyar tsoffin shugabannin kananan hukumomi na jam’iyyar PDP a jihar Jigawa, sun yi kira ga Mustapha Sule Lamido da ya shiga takarar kujerar gwamna a zaben 2023 karkashin inuwar jam’iyyar.
Kungiyar ta yi kiran ne a cikin wata takarda da ta saki a yayin taronta da ya gudana a garin Gumel da ke jihar Jigawa.
Ta bayyana cewa, kungiyar ta zauna ta yi nazarin halin da jihar Jigawa ta tsinci kanta ciki a yau, sannan ta bayyana cewa, jihar na fama da matsalolin zamantakewa da dai sauran su.
Mustapha ya kasance da ga tsohon gwamnan jihar, Alhaji Sule Lamido