Shugaban cocin INRI Evangelical Spiritual Church, Primate Elijah Ayodele, a ranar Litinin ya bayyana wasu manyan ‘yan siyasa da a ke ganin za su iya zama shugaban kasa da mataimakinsa a Najeriya a 2023.
Primate Ayodele ya bayyana sunayen gwamnonin kamar haka, Aminu Tambuwal, Nyesom Wike, Samuel Ortom, Mohammed Bala, Emmanuel Udom, Seyi Makinde, da Ifeanyi Ugwuanyi a matsayin nagartattun ‘yan takarar shugaban kasa a bangaren jam’iyyar PDP.
Ya kuma bayyana Bukola Saraki, da Peter Obi a matsayin wadanda za su iya tsayawa takara.
Mai taimaka masa kan harkokin yada labarai, Osho Oluwatosin, Primate Ayodele, ya sanya wa hannu, ya ambaci Abubakar Malami da Boss Mustapha da Kayode Fayemi da Rotimi Amaechi da Farfesa Babagana Zulum da Babatunde Raji Fashola sai Mai Mala Buni da Ibikunle Amosun da Godswill Akpabio, da kuma Rauf Aregbesola a matsayin wanda za su iya tsaya takara a matsayi shugaban kasa na jam’iyyar APC.
Ya bayyana cewa mutane da yawa za su fafata da kansu a manyan jam’iyyun siyasa biyu kuma akwai bukatar su kasance masu dabara a siyasa.
A cewar Primate Ayodele: “Wasu ‘yan siyasa an nada su ne, domin su zama shugaban kasa da mataimakin shugaban Najeriya kuma idan jam’iyyunsu su ka ba su tikitin.
“A PDP, ya ambaci Aminu Tambuwal da Nyesom Wike da Bukola Saraki da Samuel Ortom da Bala Mohammed da Emmanuel Udom tare da Seyi Makinde da kuma Ifeanyi Ugwuanyi da Peter Obi.
“A APC, akwai Abubakar Malami da Boss Mustapha da Kayode Fayemi da Rotimi Amaechi da Farfesa Babagana Zulum da Babatunde Raji Fashola sai Mai Mala Buni da Ibikunle Amosun da Godswill Akpabio da Rauf Aregbesola.”
Yanzu haka dai saura kwanaki kadan a buga ganganr siyasa a Najeriya, domin samun guraben shugabanci a matakin kasa da jihohi da kuma kananan hukumomin Najeriya a shekarar 2023.