Tsohon sakataren jam’iyyar Labour Party (LP), Kayode Ajulo, ya ce mafi yawan gwamnonin PDP da APC na goyon bayan mataimakin shugaban ƙasa, Yemi Osinbajo, wajen ganin ya gaji kujerear Buhari a 2023.
Da yake jawabi a wata hira ta cikin shirin Talabijin na Channels ‘Siyasa a yau’ Ajulo ya ce, Osinbajo ya yi abin a zo a gani cikin shekaru bakwai da suka wuce, wanda ya dace a bashi dama ya gaji Uban gidansa.
A cewarsa, ba bu wanda ya samu damar gano wani kuskuren Osinbajo, domin haka ya kamata a ba shi dama ya zama shugaban ƙasa na gaba.
Ya kuma yi kira ga jam”iyyar APC ta duba yuwuwar miƙa wa mataimakin shugaban ƙasa tikitin takara.