fidelitybank

2023: Ba na neman kujerar gwamnan Kano — Makoɗa

Date:

 

Shugaban Ma’aikatan fadar Gwamnatin Jihar Kano, Dakta Ali Haruna Makoɗa ya baiyana cewa bashi da burin tsayawa takarar kujerar gwamnan Kano a zaɓen 2023.

Makoɗa ya ƙara da cewa shi ba ya neman wata kujerar mulki a shekarar zaɓe ta 2023.

An daɗe a na raɗe-raɗin cewa Makoɗa na cikin ƴan siyasar da su ke harin babbar kujerar mulki a Kano idan kakar zaɓe ta 2023 ta zo.

Makoɗa, wanda tsohon Kwamishinan Muhalli na Jiha ne, ya baiyana hakan a yayin da ya ya ke gabatar da jawabi a wajen taron Ƙungiyar Tsofaffin Ɗaliban Makaranatar Sakandire ta Kafin Hausa, ƴan aji na shekara 1988.

Ya ce “Ali ba ya neman wata kujerar mulki a shekara ta 2023 sai kujerar da Allah ya zaɓa masa, wadda za ta zama alkhairi a gare ni da ku da duk al’ummar Jihar Kano baki ɗaya, tun da zaɓin Allah shi ne dai-dai,”

Dakta Makoɗa ya roƙi ‘ya’yan ƙungiyar da su taya su da yin addu’o’in kammala aikin da aka ɗora musu lafiya kamar yadda su ka fara lafiya.

Masoya Makoɗa  dai sun daɗe su na kiraye-kirayen ya fito neman kurejar gwamnan Jihar Kano, sabo da irin gudunmawar da su ke ganin zai iya bayarwa wajen cigaban jihar idan ya samu dama.

legitnew

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp