fidelitybank

2023: Ba na neman kujerar gwamnan Kano — Makoɗa

Date:

 

Shugaban Ma’aikatan fadar Gwamnatin Jihar Kano, Dakta Ali Haruna Makoɗa ya baiyana cewa bashi da burin tsayawa takarar kujerar gwamnan Kano a zaɓen 2023.

Makoɗa ya ƙara da cewa shi ba ya neman wata kujerar mulki a shekarar zaɓe ta 2023.

An daɗe a na raɗe-raɗin cewa Makoɗa na cikin ƴan siyasar da su ke harin babbar kujerar mulki a Kano idan kakar zaɓe ta 2023 ta zo.

Makoɗa, wanda tsohon Kwamishinan Muhalli na Jiha ne, ya baiyana hakan a yayin da ya ya ke gabatar da jawabi a wajen taron Ƙungiyar Tsofaffin Ɗaliban Makaranatar Sakandire ta Kafin Hausa, ƴan aji na shekara 1988.

Ya ce “Ali ba ya neman wata kujerar mulki a shekara ta 2023 sai kujerar da Allah ya zaɓa masa, wadda za ta zama alkhairi a gare ni da ku da duk al’ummar Jihar Kano baki ɗaya, tun da zaɓin Allah shi ne dai-dai,”

Dakta Makoɗa ya roƙi ‘ya’yan ƙungiyar da su taya su da yin addu’o’in kammala aikin da aka ɗora musu lafiya kamar yadda su ka fara lafiya.

Masoya Makoɗa  dai sun daɗe su na kiraye-kirayen ya fito neman kurejar gwamnan Jihar Kano, sabo da irin gudunmawar da su ke ganin zai iya bayarwa wajen cigaban jihar idan ya samu dama.

thisday newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mata da kanan Yara ne Ambaliya ta daidaita a jihohi 19 – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa, NEMA, ta...

Facebook ya ƙi amincewa da tsare-tsaren Turai na amfani da AI

Wasu muhimman tsare-tsare na dokokin Tarayyar Turai kan amfani...

Ranar 18 za a fara rajistar zabe – INEC

Hukumar zaɓe mai zaman kanta, INEC ta sanar da...

Trump ya tura jiragen ruwa na yaki masu dauke da makaman nukiliya kusa da Rasha

Shugaba Trump ya ce, ya umarci a matsar da...

Amnesty na tuhumar gwamnatin Najeriya kan bacewar Dadiyata

Ƙungiyar Amnesty International ta yi Allah-wadai da sakacin da...

Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansani a Kebbi

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta bayyana aniyar kafa sansaninta...

Za afara rijistar masu zabe a Najeriya – INEC

Hukumar zaɓe ta INEC, ta ce, nan gaba cikin...

Ma’aikatan Jinya sun dakatar da yajin aiki a Najeriya

Ministan lafiya a Najeriya ya ce, ma'aikatan jinya da...

Izak ya na ɗaukar horo bayan ya dage sai ya koma Liverpool

Ɗanwasan gab ana Newcastle Alexander Isak na can yana...

Masu tsaigunta wa ƴan Bindiga ne ke haddasa kashe-kashe – Gwamnan Katsina

Gwamnatin jihar Katsina ta ce masu tsegunta wa ƴanbindiga...

Gwamnoni ku yi wa mutanen ƙauyika da karkara ayyuka – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu, ya buƙaci gwamnonin ƙasar nan su...

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faɗa ADC

Tsohon ɗan jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...
X whatsapp