fidelitybank

2023: Ba na neman kujerar gwamnan Kano — Makoɗa

Date:

 

Shugaban Ma’aikatan fadar Gwamnatin Jihar Kano, Dakta Ali Haruna Makoɗa ya baiyana cewa bashi da burin tsayawa takarar kujerar gwamnan Kano a zaɓen 2023.

Makoɗa ya ƙara da cewa shi ba ya neman wata kujerar mulki a shekarar zaɓe ta 2023.

An daɗe a na raɗe-raɗin cewa Makoɗa na cikin ƴan siyasar da su ke harin babbar kujerar mulki a Kano idan kakar zaɓe ta 2023 ta zo.

Makoɗa, wanda tsohon Kwamishinan Muhalli na Jiha ne, ya baiyana hakan a yayin da ya ya ke gabatar da jawabi a wajen taron Ƙungiyar Tsofaffin Ɗaliban Makaranatar Sakandire ta Kafin Hausa, ƴan aji na shekara 1988.

Ya ce “Ali ba ya neman wata kujerar mulki a shekara ta 2023 sai kujerar da Allah ya zaɓa masa, wadda za ta zama alkhairi a gare ni da ku da duk al’ummar Jihar Kano baki ɗaya, tun da zaɓin Allah shi ne dai-dai,”

Dakta Makoɗa ya roƙi ‘ya’yan ƙungiyar da su taya su da yin addu’o’in kammala aikin da aka ɗora musu lafiya kamar yadda su ka fara lafiya.

Masoya Makoɗa  dai sun daɗe su na kiraye-kirayen ya fito neman kurejar gwamnan Jihar Kano, sabo da irin gudunmawar da su ke ganin zai iya bayarwa wajen cigaban jihar idan ya samu dama.

national news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Najeriya na neman dala biliyan 25 na bututun iskar gas zuwa Turai

Najeriya na neman dala biliyan 25 a matsayin kuɗin...

‘Yan sa-kai biyu ne suka mutu a harin da muka kai Zamfara – Sojoji

Rundunar sojin sama ta Najeirya ta tabbatar da kai...

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...
X whatsapp