Gwamnan jihar Rivers, Nyesom Wike, ya yi martani a kan kalaman da Atiku Abubakar ya yi a game da samun tikiti a jam’iyyar PDP a zaben 2023.
Jaridar Vanguard ta rawaito cewa, Nyesom Wike ya na yi wa Atiku Abubakar kaca-kaca, ya ce maganar da ya yi, ya nuna ya raina masu tsaida ‘dan takara a PDP.
Gwamnan ya fitar da jawabi a Fatakwal, jihar Ribas inda ya ce, sakamakon zaben fitar da gwanin da za a gani a jam’iyyar adawa ta PDP zai ba mutane mamaki.
Nyesom Wike ya kara da cewa, sauran ‘yan takara za su marawa wanda ya samu nasara a 2023.
Da yake magana da bakin Mai taimaka masa wajen harkokin yada labarai, Kelvin Ebiri, ya ce, Atiku ya wuce gona da iri da kalaman da aka ji daga bakinsa.