Tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar, ya halarci taron da jiga-jigan jamâiyyar PDP ta shirya a Abuja a daren ranar Litinin.
Wadanda suka halarci taron sun hada da tsohon shugaban majalisar dattawa, Bukola Saraki, gwamnan jihar Sokoto, Aminu Tambuwal da kuma jihar Bauchi, Gwamna Bala Mohammed.
Atiku yayin da yake magana bayan taron ya bayyana cewa, sun tattauna makomar PDP da Najeriya.
Tsohon mataimakin shugaban kasar a wani sako da ya wallafa a shafinsa na Facebook ya rubuta cewa âNa yi wata ganawa da Saraki da Tambuwal da Bala da Hayatudden a daren yau, domin tattauna makomar jamâiyyarmu da Najeriya. Ina fatan ci gaba da tattaunawa da gina Nigeria daya.”