Gwamnan jihar Ogun, Dapo Abiodun, a ranar Alhamis, a hukumance ya bayyana aniyarsa ta sake tsayawa takara a shekarar 2023 a karkashin jam’iyyar APC, inda ya ce har yanzu bai fidda rai ba, kuma ya jajirce wajen ganin ya cimma burin sa.
Abiodun ya bayyana hakan ne a zauren majalisar zartarwa na ofishinsa da ke Oke-Mosan Abeokuta, lokacin da ya karbi fom din tsayawa takara da ‘yan uwansa da mata suka saya masa a karkashin inuwar DA Mandate 2023.
Haka nan kuma nan take ya sanar da sake nadin mataimakiyarsa, Engr. (Mrs.) Noimot Salako-Oyedele a matsayin abokiyar takararsa.
Abiodun ya tuna yadda tafiyar ta faro ne shekaru hudu da suka gabata, inda ya yi kira ga ‘yan jihar da su hada kai da shi a wannan tafiya ta sadaukar da kai, domin gina kasa mai tsaro da wadata da tattalin arziki mai inganci da kuma goyon bayan ayyuka masu inganci da daidaito da adalci, ya ce. Abin farin ciki ne yadda mutane suka yi imani da shi kuma suka ba da goyon baya.