Gwamnatin tarayya ta ce, daukar matakan gaggawa ne suka haifar da farfadowa daga katsewar wutar lantarki a makon da ya gabata.
Ministan wutar lantarki, Engr Abubakar Aliyu ne ya bayyana haka, a lokacin da yake bayar da karin haske kan yanayin wutar lantarki a kasar nan.
A satin da ya gabata ne dai hukumar ta National grid ta ruguje har sau biyu, lamarin da ya tilastawa shugaban kasa Muhammadu Buhari mika uzuri ga ‘yan Najeriya, inda ya tabbatar da cewa an samu sauki a hanya.
‘Ministan wutar lantarki ya kira wasu masu ruwa da tsaki a harkar wutar lantarki domin kiran taron gaggawa.
A wata sanarwa da ya sanyawa hannu da kan sa ranar Asabar, Aliyu ya ce, an shawo kan lamarin.
Ya ce, an umurci Kamfanin Kasuwancin Wutar Lantarki na Najeriya Plc da ya shiga tattaunawa cikin gaggawa tare da NAOC kan yarjejeniyar sayar da makamashi na wucin gadi da nufin kawo sabuwar tashar wutar lantarki ta Okpai Il a kan grid ta yadda za ta ba da gudummawar karin ƙarfin wuta na 4OOMW na samar da wutar lantarki.