Raphael Dwamena, wanda ke taka leda a KF Egnatia ya fadi ya mutu.
Jaridar UK Mirror ta rawaito cewa matashin mai shekaru 28 ya rasu ne bayan ya yi fama da mummunar bugun zuciya.
A ranar Asabar ne tsohon dan wasan na Ghana ya fafata da Partizani Tirana, a lokacin da ya fadi a minti na 23 na wasan.
An yi watsi da wasan yayin da ma’aikatan lafiya suka yi kokarin farfado da Dwamena.
Daga karshe dai an garzaya da shi asibiti mafi kusa a garin Kavaja, amma an tabbatar da mutuwarsa jim kadan bayan isar shi bayan ya sake samun bugun zuciya.
Dwamena ya fara sanin wata matsala a zuciyarsa lokacin da aka gano a shekarar 2017.
Yana da na’urar bugun zuciya na (ICD) wanda aka saka a cikin Oktoba 2021, bayan ya fado yayin wasan Kofin Austriya.