An bukaci masu neman mukamin firaministan Pakistan, da su gabatar da takardardunsu nan da wasu sa’oi kafin cikar wa’adin gabatarwar, bayan da majalisa ta tsige Imran Khan daga mukamin.
A ranar Litinin ne ‘yan majalisar dokokin kasar za su yanke shawara a kan wanda zai gaji Imran Khan, wanda aka cire daga mukaminsa na firaminista a kuri’ar yanke kaunar da aka kada bayan abokan hadakar gwamnatinsa sun juya masa baya.
Suna dai zarginsa da tabarbarewar tattalin arzikin kasa da kuma gaza cika alkawuran da ya dauka.
Masu sharhi na ganin cewa jagoran ‘yan hamayya Shehbaz Sharif, wanda dan uwan tsohon firaministan kasar Nawaz Sharif ne, shi zai gaji kujerar firaministan.