fidelitybank

Ɗan takarar Sanatan APC na Jigawa ya rasu

Date:

Dan takarar kujerar Sanatan Jigawa ta tsakiya a jam’iyyar All Progressives Congress APC, Tijjani Ibrahim Kiyawa ya rasu.

Wata majiya mai tushe ta shaidawa DAILY POST cewa Hon. Kiyawa ya rasu ne a daren jiya da misalin karfe 11:00 na dare a wani asibitin Abuja bayan ya yi fama da rashin lafiya.

Hon. Kiyawa dai fitaccen dan siyasa ne wanda ya taba zama dan majalisar wakilai mai wakiltar Dutse da kuma mazabar Kiyawa ta tarayya daga shekarar 2011-2015 a karkashin jam’iyyar PDP.

Ya kuma kasance dan takarar gwamna a PDP a zaben 2019 wanda ya sha kaye a zaben fidda gwani a hannun Malam Aminu Ibrahim Ringim.

Kiyawa ya sauya sheka zuwa jam’iyyar All Progressives Congress, APC inda ya samu tikitin takarar sanata na jam’iyyar ta Jigawa ta tsakiya a zaben 2023 mai zuwa.

DAILY POST ta ruwaito cewa an yi garkuwa da mahaifiyarsa mai shekaru 75 Hajiya Fatima Ibrahim (Jaja) a kwanan baya a gidanta da ke garin Kiyawa.

Jami’an tsaro ne suka kubutar da ita bayan an gano ta a rukunin gidajen Danladi Nasidi da ke karamar hukumar Kumbotso a jihar Kano.

Mutuwar Kiyawa na zuwa ne kwanaki kadan bayan rasuwar kwamishinan kasuwanci da masana’antu na jihar Jigawa Salisu Zakari.

nnnhausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp