fidelitybank

Ɗan sanda na neman kotu ta rusa aurensa bisa zargin matarsa da bin maza

Date:

Wani ɗan sanda, Rafiu Ademola ɗan shekara 45 ya roƙi kotu a Igando da ta rusa aurensa da matarsa a bisa zargin ta na bin maza.

Ɗan sandan ya shaidawa kotun cewa mai-ɗakin nasa ta zama karya.

Ya kuma koka da cewa shi da idonsa ya ga irin zantukan batsa da matarsa ke yi da maza daban-daban ta WhatsApp da kuma guraren da su ke haɗuwa.

“A cikin saƙonnin da na gani har da wanda ta cewa wai ba ta da aure kuma wai a gidan yayarta ta ke zaune.

“na aika duka hirarrakin zuwa waya ta domin ya zame mini shaida,” Ademola ya shaidawa kotun.

Mai ƙarar ya ƙara da cewa matar tasa ta fiye son jiki kuma ba ta don yin girki a gidan kuma ba ta girmama mahaifansa.

A ƙarshe dai ɗan sandan ya shaidawa kotun cewa shifa yanzu ba ya son matar ta sa, inda ya roƙi kotun da ta datse igiyar auren nasu.

A na ta ɓangaren, Rashidat ta musanta duk zarge-zargen da mijin nata ya yi a kotun, amma kuma ta amince da a yanke auren.

“Ni ban taɓa bin maza ba , shine ma yanke bin mata iri-iri har ya na kawo mata cikin gidan mu na aure.

“Kwanan nan ya kore ni da ga gidan ya riƙa kuma kawo mata su na kwana a gidan,” in ji ta.

Rashidat, ƴar shekara 40 kuma mai sana’ar telanci ta shaidawa kotun cewa mijin nata ya maida ita jaka, inda ya ke jibagrta a duk sanda ya ga dama.

Kotun, wacce ta ke ƙarƙashin alƙali Adeniyi Koledoye, ya yi kira ga ma’auratan da su zauna lafiya, inda ya ɗaga zaman zuwa 16 ga watan Disamba domin yanke hukunci.

legit nig. news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...
X whatsapp