fidelitybank

Ɗan sanda na neman kotu ta rusa aurensa bisa zargin matarsa da bin maza

Date:

Wani ɗan sanda, Rafiu Ademola ɗan shekara 45 ya roƙi kotu a Igando da ta rusa aurensa da matarsa a bisa zargin ta na bin maza.

Ɗan sandan ya shaidawa kotun cewa mai-ɗakin nasa ta zama karya.

Ya kuma koka da cewa shi da idonsa ya ga irin zantukan batsa da matarsa ke yi da maza daban-daban ta WhatsApp da kuma guraren da su ke haɗuwa.

“A cikin saƙonnin da na gani har da wanda ta cewa wai ba ta da aure kuma wai a gidan yayarta ta ke zaune.

“na aika duka hirarrakin zuwa waya ta domin ya zame mini shaida,” Ademola ya shaidawa kotun.

Mai ƙarar ya ƙara da cewa matar tasa ta fiye son jiki kuma ba ta don yin girki a gidan kuma ba ta girmama mahaifansa.

A ƙarshe dai ɗan sandan ya shaidawa kotun cewa shifa yanzu ba ya son matar ta sa, inda ya roƙi kotun da ta datse igiyar auren nasu.

A na ta ɓangaren, Rashidat ta musanta duk zarge-zargen da mijin nata ya yi a kotun, amma kuma ta amince da a yanke auren.

“Ni ban taɓa bin maza ba , shine ma yanke bin mata iri-iri har ya na kawo mata cikin gidan mu na aure.

“Kwanan nan ya kore ni da ga gidan ya riƙa kuma kawo mata su na kwana a gidan,” in ji ta.

Rashidat, ƴar shekara 40 kuma mai sana’ar telanci ta shaidawa kotun cewa mijin nata ya maida ita jaka, inda ya ke jibagrta a duk sanda ya ga dama.

Kotun, wacce ta ke ƙarƙashin alƙali Adeniyi Koledoye, ya yi kira ga ma’auratan da su zauna lafiya, inda ya ɗaga zaman zuwa 16 ga watan Disamba domin yanke hukunci.

nigeria news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp