fidelitybank

Ɗan sanda na neman kotu ta rusa aurensa bisa zargin matarsa da bin maza

Date:

Wani ɗan sanda, Rafiu Ademola ɗan shekara 45 ya roƙi kotu a Igando da ta rusa aurensa da matarsa a bisa zargin ta na bin maza.

Ɗan sandan ya shaidawa kotun cewa mai-ɗakin nasa ta zama karya.

Ya kuma koka da cewa shi da idonsa ya ga irin zantukan batsa da matarsa ke yi da maza daban-daban ta WhatsApp da kuma guraren da su ke haɗuwa.

“A cikin saƙonnin da na gani har da wanda ta cewa wai ba ta da aure kuma wai a gidan yayarta ta ke zaune.

“na aika duka hirarrakin zuwa waya ta domin ya zame mini shaida,” Ademola ya shaidawa kotun.

Mai ƙarar ya ƙara da cewa matar tasa ta fiye son jiki kuma ba ta don yin girki a gidan kuma ba ta girmama mahaifansa.

A ƙarshe dai ɗan sandan ya shaidawa kotun cewa shifa yanzu ba ya son matar ta sa, inda ya roƙi kotun da ta datse igiyar auren nasu.

A na ta ɓangaren, Rashidat ta musanta duk zarge-zargen da mijin nata ya yi a kotun, amma kuma ta amince da a yanke auren.

“Ni ban taɓa bin maza ba , shine ma yanke bin mata iri-iri har ya na kawo mata cikin gidan mu na aure.

“Kwanan nan ya kore ni da ga gidan ya riƙa kuma kawo mata su na kwana a gidan,” in ji ta.

Rashidat, ƴar shekara 40 kuma mai sana’ar telanci ta shaidawa kotun cewa mijin nata ya maida ita jaka, inda ya ke jibagrta a duk sanda ya ga dama.

Kotun, wacce ta ke ƙarƙashin alƙali Adeniyi Koledoye, ya yi kira ga ma’auratan da su zauna lafiya, inda ya ɗaga zaman zuwa 16 ga watan Disamba domin yanke hukunci.

www.nigerianews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojojin hadin gwiwa sun hallaka ‘yan Boko Haram a tafkin Chadi

Rundunar hadin gwiwa mai yaƙi da Boko Haram a...

Na yi rashin aboki na gari kuma Najeriya ta rasa mutumin kirki – Tinubu

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, na ci gaba da alhinin...

Shettima ya jagoranci yi wa Buhari addu’o’i na musamman a Daura

An gudanar da addu'o'i na musamman don neman gafara...

Isra’ila ta kashe mana fararen hula – Syria

Shugaban Syria, Ahmed al-Sharaa ya zargi Isra'ila da kai...

Za mu koma fadar gwamnatin Katsina mu karbi gaisuwar Buhari – Radda

Gwamnan jihar Katsina, Dikko Umar Radda ya ce bayan...

Tinubu zai jagoranci yi wa Buhari addu’a

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, zai jagoranci taron addu'o'i na...

Muƙarraban Buhari sun ci amanar da ya ba su lokacin mulkinsa – Bagos

Wani tsohon ɗan majalisar wakilai, Dachung Bagos ya bayyana...

Guardiola ya bude kofa ga ‘yan wasa shida su bar kungiyar

Kocin Manchester City, Pep Guardiola, a shirye yake ya...

Ba gudu ba ja da baya a zanga-zangar mu – Tsofaffin ‘Yansanda

Kungiyar ‘yan sandan Najeriya masu ritaya ta sanar da...

Malami ya magantu kan sukar rashawa a mulkin marigayi Buhari

Tsohon babban Lauyan Najeriya kuma ministan shari'a, Abubakar Malami,...

Turkiyya ta gargadi Najeriya kan ‘yan ta’addar FETO

Gwamnatin Turkiyya ta fitar da wani gargadin cewa, mambobin...

Kiristoci sun jinjinawa Musulmai yadda aka yi jana’izar Buhari ba kashe kudi

Ana samun karuwar al’ummar Kudancin Najeriya musamman mabiya addinin...
X whatsapp