fidelitybank

Ɗan Pantami ya shaƙi iskar ƴanci sa’o’i 24 bayan sace shi

Date:

 

 

 

Ali Isa Ali, ɗan Ministan Sadarwa da Tattalin Arziki ta Fasahar Zamani, Isa Ali Pantami, ya shaƙi iskar ƴanci, sa’o’i 24 bayan da a ka ce an sace shi.

Jaridar Nation ta rawaito cewa an tsinci Ali, ɗan shekara 14 a wani shingen binciken jami’an tsaro a Ƙaramar Hukumar Dambam, Jihar Bauchi.

An rawaito cewa an yi garkuwa da Ali ne a kan hanyar shi ta dawowa gida bayan an tashe su da ga makarantar islamiyya, inda masu garkuwar da shi su ka yi awon-gaba da shi a kan babur.

Jaridar ta ce babu wani cikakken bayani kan yadda yaron ya kuɓuta, inda ya ke zaune wajen mahaifiyarsa a Bauchi bayan da a ke zargin sun rabu da Pantami.

Nation ta ƙara da cewa mahaifiyar taron ma ta tabbatar da kubutar ta sa, inda ta ce tuni ya na gida tare da ita.

Haka shima Babban Limamin Masallacin Juma’a na Isa Ali, Imam Hussain ya tabbatar da cewa Ali ya kuɓuta kuma ya na wajen mahaifiyarsa.

Jaridar ta ƙarar da cewa da a ka tuntuɓi Kwamishinan Ƴan Sanda na Jihar Bauchi, Ahmed Mohammed Wakil, ya ce bashi da masaniyar sace yaron sabo da ba a kai rahoton ga ƴan sanda ba.

Ya ce ya tuntuɓi caji-ofisoshi cikin garin Bauchi amma duk sun ce basu da masaniya kan lamarin.

www.nigeriannewspapers.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...
X whatsapp